- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
circa 1446–1406 BC
The Wilderness Years
Forty years of wandering in the desert test Israel's faith and prepare a new generation to enter the promised land.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Maimaitawar Shari’a 5:27kusan 1451 K.H.
Kai, ka matsa kusa, ka saurara ga dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa. Sa’an nan ka faɗa mana dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu saurara, mu kuma yi biyayya.”
- Maimaitawar Shari’a 5:28kusan 1451 K.H.
Ubangiji ya ji ku, sa’ad da kuka yi magana da ni, sai Ubangiji ya ce mini, “Na ji abin da wannan mutane suka faɗa maka. Abin da suka faɗa daidai ne.
- Maimaitawar Shari’a 5:29kusan 1451 K.H.
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma ’ya’yansu har abada!
- Maimaitawar Shari’a 5:30kusan 1451 K.H.
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
- Maimaitawar Shari’a 5:31kusan 1451 K.H.
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
- Maimaitawar Shari’a 5:32kusan 1451 K.H.
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
- Maimaitawar Shari’a 5:33kusan 1451 K.H.
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.
- Maimaitawar Shari’a 6:1kusan 1451 K.H.
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
- Maimaitawar Shari’a 6:2kusan 1451 K.H.
saboda ku, ’ya’yanku, da kuma ’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
- Maimaitawar Shari’a 6:3kusan 1451 K.H.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
- Maimaitawar Shari’a 6:4kusan 1451 K.H.
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
- Maimaitawar Shari’a 6:5kusan 1451 K.H.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
- Maimaitawar Shari’a 6:6kusan 1451 K.H.
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
- Maimaitawar Shari’a 6:7kusan 1451 K.H.
Ku koya wa ’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
- Maimaitawar Shari’a 6:8kusan 1451 K.H.
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
- Maimaitawar Shari’a 6:9kusan 1451 K.H.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
- Maimaitawar Shari’a 6:10kusan 1451 K.H.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
- Maimaitawar Shari’a 6:11kusan 1451 K.H.
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
- Maimaitawar Shari’a 6:12kusan 1451 K.H.
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
- Maimaitawar Shari’a 6:13kusan 1451 K.H.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
- Maimaitawar Shari’a 6:14kusan 1451 K.H.
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
- Maimaitawar Shari’a 6:15kusan 1451 K.H.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
- Maimaitawar Shari’a 6:16kusan 1451 K.H.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
- Maimaitawar Shari’a 6:17kusan 1451 K.H.
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
- Maimaitawar Shari’a 6:18kusan 1451 K.H.
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.