Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 1:27kusan 5 K.H.

    gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.

  2. Luka 1:28kusan 5 K.H.

    Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”

  3. Luka 1:29kusan 5 K.H.

    Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?

  4. Luka 1:30kusan 5 K.H.

    Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.

  5. Luka 1:31kusan 5 K.H.

    Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.

  6. Luka 1:32kusan 5 K.H.

    Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,

  7. Luka 1:33kusan 5 K.H.

    zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.”

  8. Luka 1:34kusan 5 K.H.

    Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”

  9. Luka 1:35kusan 5 K.H.

    Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.

  10. Luka 1:36kusan 5 K.H.

    ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.

  11. Luka 1:37kusan 5 K.H.

    Gama ba abin da zai gagari Allah.”

  12. Luka 1:38kusan 5 K.H.

    Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.

  13. Luka 1:39kusan 5 K.H.

    A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,

  14. Luka 1:40kusan 5 K.H.

    inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.

  15. Luka 1:41kusan 5 K.H.

    Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.

  16. Luka 1:42kusan 5 K.H.

    Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!

  17. Luka 1:43kusan 5 K.H.

    Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?

  18. Luka 1:44kusan 5 K.H.

    Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.

  19. Luka 1:45kusan 5 K.H.

    Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”

  20. Luka 1:46kusan 5 K.H.

    Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji

  21. Luka 1:47kusan 5 K.H.

    ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,

  22. Luka 1:48kusan 5 K.H.

    gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,

  23. Luka 1:49kusan 5 K.H.

    gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.

  24. Luka 1:50kusan 5 K.H.

    Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.

  25. Luka 1:51kusan 5 K.H.

    Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.