circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 1:27kusan 5 K.H.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
- Luka 1:28kusan 5 K.H.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
- Luka 1:29kusan 5 K.H.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
- Luka 1:30kusan 5 K.H.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
- Luka 1:31kusan 5 K.H.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
- Luka 1:32kusan 5 K.H.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
- Luka 1:33kusan 5 K.H.
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.”
- Luka 1:34kusan 5 K.H.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
- Luka 1:35kusan 5 K.H.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
- Luka 1:36kusan 5 K.H.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
- Luka 1:37kusan 5 K.H.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
- Luka 1:38kusan 5 K.H.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
- Luka 1:39kusan 5 K.H.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
- Luka 1:40kusan 5 K.H.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
- Luka 1:41kusan 5 K.H.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
- Luka 1:42kusan 5 K.H.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
- Luka 1:43kusan 5 K.H.
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
- Luka 1:44kusan 5 K.H.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
- Luka 1:45kusan 5 K.H.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
- Luka 1:46kusan 5 K.H.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
- Luka 1:47kusan 5 K.H.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
- Luka 1:48kusan 5 K.H.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
- Luka 1:49kusan 5 K.H.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
- Luka 1:50kusan 5 K.H.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
- Luka 1:51kusan 5 K.H.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.