circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Luka 1:52kusan 5 K.H.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
- Luka 1:53kusan 5 K.H.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
- Luka 1:54kusan 5 K.H.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
- Luka 1:55kusan 5 K.H.
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.”
- Luka 1:56kusan 5 K.H.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
- Luka 1:57kusan 5 K.H.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
- Luka 1:58kusan 5 K.H.
Maƙwabtanta da ’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
- Luka 1:59kusan 5 K.H.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
- Luka 1:60kusan 5 K.H.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
- Luka 1:61kusan 5 K.H.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
- Luka 1:62kusan 5 K.H.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
- Luka 1:63kusan 5 K.H.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
- Luka 1:64kusan 5 K.H.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
- Luka 1:65kusan 5 K.H.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
- Luka 1:66kusan 5 K.H.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
- Luka 1:67kusan 5 K.H.
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
- Luka 1:68kusan 5 K.H.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
- Luka 1:69kusan 5 K.H.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
- Luka 1:70kusan 5 K.H.
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),
- Luka 1:71kusan 5 K.H.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
- Luka 1:72kusan 5 K.H.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
- Luka 1:73kusan 5 K.H.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
- Luka 1:74kusan 5 K.H.
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
- Luka 1:75kusan 5 K.H.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
- Luka 1:76kusan 5 K.H.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,