Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 1:52kusan 5 K.H.

    Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.

  2. Luka 1:53kusan 5 K.H.

    Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.

  3. Luka 1:54kusan 5 K.H.

    Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai

  4. Luka 1:55kusan 5 K.H.

    ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.”

  5. Luka 1:56kusan 5 K.H.

    Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.

  6. Luka 1:57kusan 5 K.H.

    Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.

  7. Luka 1:58kusan 5 K.H.

    Maƙwabtanta da ’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.

  8. Luka 1:59kusan 5 K.H.

    A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,

  9. Luka 1:60kusan 5 K.H.

    amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”

  10. Luka 1:61kusan 5 K.H.

    Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”

  11. Luka 1:62kusan 5 K.H.

    Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.

  12. Luka 1:63kusan 5 K.H.

    Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.

  13. Luka 1:64kusan 5 K.H.

    Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.

  14. Luka 1:65kusan 5 K.H.

    Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.

  15. Luka 1:66kusan 5 K.H.

    Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.

  16. Luka 1:67kusan 5 K.H.

    Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,

  17. Luka 1:68kusan 5 K.H.

    “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.

  18. Luka 1:69kusan 5 K.H.

    Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda

  19. Luka 1:70kusan 5 K.H.

    (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),

  20. Luka 1:71kusan 5 K.H.

    cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu

  21. Luka 1:72kusan 5 K.H.

    don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,

  22. Luka 1:73kusan 5 K.H.

    rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,

  23. Luka 1:74kusan 5 K.H.

    don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,

  24. Luka 1:75kusan 5 K.H.

    cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.

  25. Luka 1:76kusan 5 K.H.

    “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,