Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 2:22kusan 4 M.

    Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji

  2. Luka 2:23kusan 4 M.

    (yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),

  3. Luka 2:24kusan 4 M.

    don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko ’yan tattabarai biyu.”

  4. Luka 2:25kusan 4 M.

    To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.

  5. Luka 2:26kusan 4 M.

    An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.

  6. Luka 2:27kusan 4 M.

    Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,

  7. Luka 2:28kusan 4 M.

    sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,

  8. Luka 2:29kusan 4 M.

    “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.

  9. Luka 2:30kusan 4 M.

    Gama idanuna sun ga cetonka,

  10. Luka 2:31kusan 4 M.

    wanda ka shirya a gaban dukan mutane,

  11. Luka 2:32kusan 4 M.

    haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”

  12. Luka 2:33kusan 4 M.

    Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.

  13. Luka 2:34kusan 4 M.

    Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,

  14. Luka 2:35kusan 4 M.

    ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”

  15. Luka 2:36kusan 4 M.

    Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,

  16. Luka 2:37kusan 4 M.

    ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.

  17. Luka 2:38kusan 4 M.

    Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.

  18. Luka 2:39kusan 4 M.

    Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.

  19. Luka 2:40kusan 4 M.

    Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.

  20. Luka 2:41kusan 8 M.

    Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.

  21. Luka 2:42kusan 8 M.

    Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.

  22. Luka 2:43kusan 8 M.

    Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.

  23. Luka 2:44kusan 8 M.

    Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin ’yan’uwansu da abokansu.

  24. Luka 2:45kusan 8 M.

    Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.

  25. Luka 2:46kusan 8 M.

    Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.