Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 3:20kusan 26 M.

    Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.

  2. Luka 3:21kusan 26 M.

    Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,

  3. Luka 3:22kusan 26 M.

    Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”

  4. Luka 3:23kusan 26 M.

    To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,

  5. Luka 3:24kusan 26 M.

    ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,

  6. Luka 3:25kusan 26 M.

    ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,

  7. Luka 3:26kusan 26 M.

    ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,

  8. Luka 3:27kusan 26 M.

    ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,

  9. Luka 3:28kusan 26 M.

    ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,

  10. Luka 3:29kusan 26 M.

    ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,

  11. Luka 3:30kusan 26 M.

    ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,

  12. Luka 3:31kusan 26 M.

    ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,

  13. Luka 3:32kusan 26 M.

    ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,

  14. Luka 3:33kusan 26 M.

    ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,

  15. Luka 3:34kusan 26 M.

    ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,

  16. Luka 3:35kusan 26 M.

    ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,

  17. Luka 3:36kusan 26 M.

    ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,

  18. Luka 3:37kusan 26 M.

    ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,

  19. Luka 3:38kusan 26 M.

    ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.

  20. Luka 4:1kusan 27 M.

    Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,

  21. Luka 4:2kusan 27 M.

    inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.

  22. Luka 4:3kusan 27 M.

    Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”

  23. Luka 4:4kusan 27 M.

    Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”

  24. Luka 4:5kusan 27 M.

    Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.

  25. Luka 4:6kusan 27 M.

    Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.