circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Yohanna 7:42kusan 33 M.
Nassi bai ce Kiristi zai fito daga zuriyar Dawuda, daga kuma Betlehem garin da Dawuda ya zauna ba?”
- Yohanna 7:43kusan 33 M.
Sai mutanen suka rabu saboda Yesu.
- Yohanna 7:44kusan 33 M.
Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
- Yohanna 7:45kusan 33 M.
A ƙarshe masu gadin haikali suka koma wurin manyan firistocin da Farisiyawa, waɗanda suka tambaye su cewa, “Don me ba ku kawo shi nan ba?”
- Yohanna 7:46kusan 33 M.
Sai masu gadin suka ce, “Kai, babu wanda ya taɓa magana kamar wannan mutum.”
- Yohanna 7:47kusan 33 M.
Sai Farisiyawa suka amsa cikin fushi suka ce, “Af, kuna nufi har da ku ma ya ruɗe ku ke nan?
- Yohanna 7:48kusan 33 M.
Akwai wani daga cikin masu mulki ko cikin Farisiyawan da ya gaskata da shi?
- Yohanna 7:49kusan 33 M.
A’a! Sai dai wannan taron da ba su san kome game da Doka ba, la’anannu ne.”
- Yohanna 7:50kusan 33 M.
Nikodimus, wanda ya je wurin Yesu dā, wanda kuma yake ɗayansu ya ce,
- Yohanna 7:51kusan 33 M.
“Ashe, dokarmu takan hukunta mutum ba tare da an fara ji daga bakinsa game da abin da yake yi ba?”
- Yohanna 7:52kusan 33 M.
Sai suka amsa suka ce, “Kai ma daga Galili ne? Bincika ka gani, za ka iske cewa ba annabin da zai fito daga Galili.”
- Yohanna 7:53kusan 33 M.
Sai kowannensu ya koma gidansa.
- Yohanna 8:1kusan 33 M.
Amma Yesu ya tafi Dutsen Zaitun.
- Yohanna 8:2kusan 33 M.
Da sassafe ya sāke bayyana a filin haikali, inda dukan mutane suka taru kewaye da shi, sai ya zauna don yă koya musu.
- Yohanna 8:3kusan 33 M.
Sai malaman dokoki da Farisiyawa suka kawo wata macen da aka kama a zina. Suka sa ta tsaya a gaban taron
- Yohanna 8:4kusan 33 M.
suka kuma ce wa Yesu, “Malam, an kama wannan mace tana zina.
- Yohanna 8:5kusan 33 M.
A cikin Doka Musa ya umarce mu, mu jajjefe irin waɗannan mata. To, me ka ce?”
- Yohanna 8:6kusan 33 M.
Sun yi wannan tambaya ce don su sa masa tarko, don su sami hanyar zarge shi. Amma Yesu ya sunkuya ya fara rubutu a ƙasa da yatsarsa.
- Yohanna 8:7kusan 33 M.
Da suka ci gaba da yin masa tambayoyi, sai ya miƙe tsaye ya ce musu, “In da wani a cikinku da ba shi da zunubi, sai yă fara jifanta da dutse.”
- Yohanna 8:8kusan 33 M.
Sai ya sāke sunkuyawa ya kuma yi rubutu a ƙasa.
- Yohanna 8:9kusan 33 M.
Da jin haka, waɗanda suka ji sai suka fara tashi daga wurin ɗaya-ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, sai da aka bar Yesu kaɗai, tare da macen tsaye a wurin.
- Yohanna 8:10kusan 33 M.
Sai Yesu ya miƙe tsaye ya tambaye ta ya ce, “Mace, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?”
- Yohanna 8:11kusan 33 M.
Ta ce, “Ba kowa, ranka yă daɗe.” Sai Yesu ya ce, “Haka ni ma ban hukunta ki ba. Ki tafi, ki daina rayuwar zunubi.”
- Yohanna 8:12kusan 33 M.
Sa’ad da Yesu ya sāke magana da mutanen, sai ya ce, “Ni ne hasken duniya. Duk wanda ya bi ni ba zai yi tafiya cikin duhu ba, sai dai yă sami hasken rayuwa.”
- Yohanna 8:13kusan 33 M.
Sai Farisiyawa suka tambaye shi suka ce, “Ga kai dai, kana yi wa kanka shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.”