circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Yohanna 6:63kusan 32 M.
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
- Yohanna 6:64kusan 32 M.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
- Yohanna 6:65kusan 32 M.
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
- Yohanna 6:66kusan 32 M.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
- Yohanna 6:67kusan 32 M.
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
- Yohanna 6:68kusan 32 M.
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami.
- Yohanna 6:69kusan 32 M.
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
- Yohanna 6:70kusan 32 M.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
- Yohanna 6:71kusan 32 M.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)
- Yohanna 7:1kusan 33 M.
Bayan wannan, sai Yesu ya yi ta zagawa a cikin Galili, da ganga bai yarda yă je Yahudiya ba domin Yahudawa a can suna nema su kashe shi.
- Yohanna 7:2kusan 33 M.
Amma sa’ad da Bikin Tabanakul na Yahudawa ya yi kusa,
- Yohanna 7:3kusan 33 M.
sai ’yan’uwan Yesu suka ce masa, “Ya kamata ka bar nan ka tafi Yahudiya, don almajiranka su ga ayyukan banmamaki da kake yi.
- Yohanna 7:4kusan 33 M.
Ba wanda yake so a san shi da zai yi abu a ɓoye. Da yake kana yin waɗannan abubuwa, sai ka nuna kanka ga duniya.”
- Yohanna 7:5kusan 33 M.
Domin ko ’yan’uwansa ma ba su gaskata da shi ba.
- Yohanna 7:6kusan 33 M.
Saboda haka Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna; amma a gare ku kowane lokaci daidai ne.
- Yohanna 7:7kusan 33 M.
Duniya ba za tă iya ƙinku ba, amma ni take ƙi domin ina shaida cewa ayyukanta mugaye ne.
- Yohanna 7:8kusan 33 M.
Ku ku tafi Bikin, ba zan haura zuwa wannan Bikin ba yanzu, domin lokacina bai yi ba tukuna.”
- Yohanna 7:9kusan 33 M.
Da ya faɗa haka, sai ya dakata a Galili.
- Yohanna 7:10kusan 33 M.
Amma fa, bayan ’yan’uwansa suka tafi Bikin, shi ma ya tafi, ba a fili ba, amma a ɓoye.
- Yohanna 7:11kusan 33 M.
A Bikin kuwa, Yahudawa suka yi ta nemansa, suna cewa, “Ina mutumin yake?”
- Yohanna 7:12kusan 33 M.
A cikin taron kuwa aka yi ta raɗe-raɗe game da shi. Waɗansu suka ce, “Shi mutumin kirki ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “A’a, ai, ruɗin mutane yake.”
- Yohanna 7:13kusan 33 M.
Amma ba wanda ya ce kome a fili game da shi don tsoron Yahudawa.
- Yohanna 7:14kusan 33 M.
Sai bayan da aka kai tsakiyar Bikin, sa’an nan Yesu ya haura zuwa filin haikali ya fara koyarwa.
- Yohanna 7:15kusan 33 M.
Yahudawa suka yi mamaki suna tambaya, “Yaya wannan mutum ya sami wannan sani haka ba tare da ya yi wani karatu ba?”
- Yohanna 7:16kusan 33 M.
Yesu ya amsa ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta fito ne daga wurin wanda ya aiko ni.