Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Yohanna 6:13kusan 32 M.

    Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.

  2. Yohanna 6:14kusan 32 M.

    Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”

  3. Yohanna 6:15kusan 32 M.

    Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.

  4. Yohanna 6:16kusan 32 M.

    Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,

  5. Yohanna 6:17kusan 32 M.

    inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.

  6. Yohanna 6:18kusan 32 M.

    Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.

  7. Yohanna 6:19kusan 32 M.

    Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.

  8. Yohanna 6:20kusan 32 M.

    Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”

  9. Yohanna 6:21kusan 32 M.

    Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.

  10. Yohanna 6:22kusan 32 M.

    Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.

  11. Yohanna 6:23kusan 32 M.

    Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.

  12. Yohanna 6:24kusan 32 M.

    Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.

  13. Yohanna 6:25kusan 32 M.

    Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”

  14. Yohanna 6:26kusan 32 M.

    Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.

  15. Yohanna 6:27kusan 32 M.

    Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.”

  16. Yohanna 6:28kusan 32 M.

    Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”

  17. Yohanna 6:29kusan 32 M.

    Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”

  18. Yohanna 6:30kusan 32 M.

    Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?

  19. Yohanna 6:31kusan 32 M.

    Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”

  20. Yohanna 6:32kusan 32 M.

    Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.

  21. Yohanna 6:33kusan 32 M.

    Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”

  22. Yohanna 6:34kusan 32 M.

    Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”

  23. Yohanna 6:35kusan 32 M.

    Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.

  24. Yohanna 6:36kusan 32 M.

    Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.

  25. Yohanna 6:37kusan 32 M.

    Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.