Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Yohanna 6:38kusan 32 M.

    Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.

  2. Yohanna 6:39kusan 32 M.

    Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.

  3. Yohanna 6:40kusan 32 M.

    Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.”

  4. Yohanna 6:41kusan 32 M.

    Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”

  5. Yohanna 6:42kusan 32 M.

    Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’ ”

  6. Yohanna 6:43kusan 32 M.

    Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.

  7. Yohanna 6:44kusan 32 M.

    Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.

  8. Yohanna 6:45kusan 32 M.

    A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.

  9. Yohanna 6:46kusan 32 M.

    Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.

  10. Yohanna 6:47kusan 32 M.

    Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami.

  11. Yohanna 6:48kusan 32 M.

    Ni ne burodin rai.

  12. Yohanna 6:49kusan 32 M.

    Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.

  13. Yohanna 6:50kusan 32 M.

    Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.

  14. Yohanna 6:51kusan 32 M.

    Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.”

  15. Yohanna 6:52kusan 32 M.

    Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”

  16. Yohanna 6:53kusan 32 M.

    Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.

  17. Yohanna 6:54kusan 32 M.

    Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.

  18. Yohanna 6:55kusan 32 M.

    Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.

  19. Yohanna 6:56kusan 32 M.

    Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.

  20. Yohanna 6:57kusan 32 M.

    Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.

  21. Yohanna 6:58kusan 32 M.

    Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.”

  22. Yohanna 6:59kusan 32 M.

    Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.

  23. Yohanna 6:60kusan 32 M.

    Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”

  24. Yohanna 6:61kusan 32 M.

    Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?

  25. Yohanna 6:62kusan 32 M.

    Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!