circa 6 BC – AD 30
The Life of Jesus
The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.
Ayoyi daga wannan lokacin
- Yohanna 8:14kusan 33 M.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, gama na san inda na fito da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ko inda za ni ba.
- Yohanna 8:15kusan 33 M.
Kuna shari’a bisa ga ma’aunin mutane; ni kuwa ba na yin wa kowa shari’a.
- Yohanna 8:16kusan 33 M.
Amma ko da zan yi shari’a, shari’ata daidai ce, don ba ni kaɗai ba ne. Ina tare da Uba da ya aiko ni.
- Yohanna 8:17kusan 33 M.
A cikin Dokarku a rubuce yake cewa shaidar mutum biyu tabbatacciya ce.
- Yohanna 8:18kusan 33 M.
Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.”
- Yohanna 8:19kusan 33 M.
Suka tambaye shi suka ce, “Ina Uban nan naka?” Sai Yesu ya ce, “Ba ku san ni ko Ubana ba. Da kun san ni, da za ku san Ubana ma.”
- Yohanna 8:20kusan 33 M.
Ya faɗi waɗannan kalmomi ne yayinda yake koyarwa a filin haikali, kusa da inda ake ajiye baye-baye. Duk da haka ba wanda ya kama shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna.
- Yohanna 8:21kusan 33 M.
Har wa yau Yesu ya sāke ce musu, “Zan tafi, za ku kuwa neme ni, za ku kuma mutu cikin zunubinku. Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba.”
- Yohanna 8:22kusan 33 M.
Wannan ya sa Yahudawa suka yi tambaya suka ce, “Zai kashe kansa ne? Shi ya sa yake cewa, ‘Inda za ni, ba za ku iya zuwa ba’?”
- Yohanna 8:23kusan 33 M.
Amma ya ci gaba da cewa, “Ku daga ƙasa kuke; ni kuwa daga bisa ne. Ku na duniyan nan ne; ni kuwa ba na duniyan nan ba ne.
- Yohanna 8:24kusan 33 M.
Na gaya muku cewa za ku mutu cikin zunubanku; in ba ku gaskata cewa ni ne wanda na ce nake ba, lalle za ku mutu cikin zunubanku.”
- Yohanna 8:25kusan 33 M.
Suka ce, “Wane ne kai?” Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ne wannan da na sha faɗi muku.
- Yohanna 8:26kusan 33 M.
Ina da abubuwa masu yawa da zan faɗa game ku in kuma yi muku shari’a. Amma wanda ya aiko ni mai aminci ne, abin da kuma na ji daga gare shi, shi nake gaya wa duniya.”
- Yohanna 8:27kusan 33 M.
Ba su gane cewa yana yin musu magana game da Ubansa ba ne.
- Yohanna 8:28kusan 33 M.
Saboda haka Yesu ya ce, “Sa’ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa’an nan ne za ku san cewa ni ne wannan da na ce nake. Ni kuwa ba na yin kome ni kaɗai, sai in dai faɗi abin da Uba ya koya mini.
- Yohanna 8:29kusan 33 M.
Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni; bai bar ni ni kaɗai ba, domin kullum ina aikata abin da ya gamshe shi.”
- Yohanna 8:30kusan 33 M.
Sa’ad da yake cikin magana, da yawa suka ba da gaskiya gare shi.
- Yohanna 8:31kusan 33 M.
Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
- Yohanna 8:32kusan 33 M.
Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă ’yantar da ku.”
- Yohanna 8:33kusan 33 M.
Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a ’yantar da mu?”
- Yohanna 8:34kusan 33 M.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
- Yohanna 8:35kusan 33 M.
Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada.
- Yohanna 8:36kusan 33 M.
Saboda haka in Ɗan ya ’yantar da ku, za ku ’yantu da gaske.
- Yohanna 8:37kusan 33 M.
Na dai san ku zuriyar Ibrahim ne. Duk da haka kuna shiri ku kashe ni, don maganata ba ta da wurin zama a cikinku.
- Yohanna 8:38kusan 33 M.
Ina faɗi muku abin da na gani a wurin Ubana, ku kuwa kuna yin abin da kuka ji daga wurin ubanku.”