Tsallake zuwa abun ciki

Karin Magana23

Hankali yayin cin abinci tare da masu mulki

1
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.

Wawancin bin dukiya

4
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.

Ka guji mai rowa da mai mugunta

6
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.

Hikima ga masu sauraro dabam-dabam

9
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.

Girmama iyaka da matalauta

10
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.

Miƙa kai ga koyarwa

12
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa.
15
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.

Kada ka yi kishin masu zunubi

17
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.

Guje wa maye da kwaɗayi

19
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!

Haɗarin lalatar jima’i

26
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28
Kamar ’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.

Jerin wahalolin maye

29
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
Use arrow keys to navigate
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options