Tsallake zuwa abun ciki

circa 605–538 BC

The Babylonian Exile

Jerusalem falls and the temple burns; Ezekiel and Daniel minister among the exiles as Lamentations mourns the city's ruin.

1,784 ayoyi · 3 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Ezekiyel 1:22kusan 595 K.H.

    A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.

  2. Ezekiyel 1:23kusan 595 K.H.

    A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.

  3. Ezekiyel 1:24kusan 595 K.H.

    Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.

  4. Ezekiyel 1:25kusan 595 K.H.

    Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.

  5. Ezekiyel 1:26kusan 595 K.H.

    A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.

  6. Ezekiyel 1:27kusan 595 K.H.

    Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.

  7. Ezekiyel 1:28kusan 595 K.H.

    Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.

  8. Ezekiyel 2:1kusan 595 K.H.

    Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”

  9. Ezekiyel 2:2kusan 595 K.H.

    Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.

  10. Ezekiyel 2:3kusan 595 K.H.

    Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar ’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.

  11. Ezekiyel 2:4kusan 595 K.H.

    Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’

  12. Ezekiyel 2:5kusan 595 K.H.

    Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.

  13. Ezekiyel 2:6kusan 595 K.H.

    Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.

  14. Ezekiyel 2:7kusan 595 K.H.

    Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su ’yan tawaye ne.

  15. Ezekiyel 2:8kusan 595 K.H.

    Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan ’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”

  16. Ezekiyel 2:9kusan 595 K.H.

    Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,

  17. Ezekiyel 2:10kusan 595 K.H.

    wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.

  18. Ezekiyel 3:1kusan 595 K.H.

    Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”

  19. Ezekiyel 3:2kusan 595 K.H.

    Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.

  20. Ezekiyel 3:3kusan 595 K.H.

    Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.

  21. Ezekiyel 3:4kusan 595 K.H.

    Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.

  22. Ezekiyel 3:5kusan 595 K.H.

    Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,

  23. Ezekiyel 3:6kusan 595 K.H.

    ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.

  24. Ezekiyel 3:7kusan 595 K.H.

    Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.

  25. Ezekiyel 3:8kusan 595 K.H.

    Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.