Tsallake zuwa abun ciki

circa 1380–1050 BC

The Judges & Ruth

Israel cycles through rebellion, oppression, and rescue under charismatic leaders—culminating in Ruth's faithful love story.

703 ayoyi · 2 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Mahukunta 9:31kusan 1233 K.H.

    Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da ’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.

  2. Mahukunta 9:32kusan 1233 K.H.

    To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.

  3. Mahukunta 9:33kusan 1233 K.H.

    Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”

  4. Mahukunta 9:34kusan 1233 K.H.

    Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.

  5. Mahukunta 9:35kusan 1233 K.H.

    To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.

  6. Mahukunta 9:36kusan 1233 K.H.

    Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”

  7. Mahukunta 9:37kusan 1233 K.H.

    Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”

  8. Mahukunta 9:38kusan 1233 K.H.

    Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”

  9. Mahukunta 9:39kusan 1233 K.H.

    Saboda haka Ga’al ya fito da ’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.

  10. Mahukunta 9:40kusan 1233 K.H.

    Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.

  11. Mahukunta 9:41kusan 1233 K.H.

    Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da ’yan’uwansa daga Shekem.

  12. Mahukunta 9:42kusan 1233 K.H.

    Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.

  13. Mahukunta 9:43kusan 1233 K.H.

    Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.

  14. Mahukunta 9:44kusan 1233 K.H.

    Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.

  15. Mahukunta 9:45kusan 1233 K.H.

    Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.

  16. Mahukunta 9:46kusan 1233 K.H.

    Da jin haka, sai ’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.

  17. Mahukunta 9:47kusan 1233 K.H.

    Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,

  18. Mahukunta 9:48kusan 1233 K.H.

    sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”

  19. Mahukunta 9:49kusan 1233 K.H.

    Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.

  20. Mahukunta 9:50kusan 1233 K.H.

    Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.

  21. Mahukunta 9:51kusan 1233 K.H.

    A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.

  22. Mahukunta 9:52kusan 1233 K.H.

    Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,

  23. Mahukunta 9:53kusan 1233 K.H.

    sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.

  24. Mahukunta 9:54kusan 1233 K.H.

    Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’ ” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.

  25. Mahukunta 9:55kusan 1233 K.H.

    Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.