Skip to content

Naphtali

49 ayoyi · 18 'yan gida

An kuma san shi da: Nephthalim

Ayoyin da suka ambaci Naphtali

Tace bisa littafi
  1. Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da ’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.

  2. ’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.

  3. ’Ya’yan Naftali maza su ne, Yazeyel, Guni, Yezer da Shillem.

  4. “Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan ’ya’ya.

  5. Dan da Naftali; Gad da Asher.

  6. daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”

  7. Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.

  8. Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.

  9. Kabilar Naftali za su zama na biye da su. Shugaban mutanen kuwa shi ne Ahira ɗan Enan.

  10. A rana ta goma sha biyu, Ahira ɗan Enan, shugaban mutanen Naftali, ya kawo hadayarsa.

  11. Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.

  12. Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;

  13. Zuriyar Naftali bisa ga kabilansu, daga Yazeyel, kabilar Yazeyelawa; daga Guni, kabilar Guniyawa;

  14. Waɗannan su ne kabilan Naftali, jimillarsu ta kai 45,400.

  15. Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”

  16. Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.

  17. Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”

  18. da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,

  19. Ƙuri’a ta shida ta fāɗa a kan kabilar Naftali, bisa ga iyalansu.

  20. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Naftali ta samu, bisa ga iyalansu.

  21. Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.

  22. Aka kuma ba wa zuriyar Gershon garuruwa goma sha uku daga iyalan kabilan Issakar, Asher, Naftali, da kuma rabin kabilar Manasse a Bashan.

  23. daga kabilar Naftali kuma aka ba su, Kedesh a cikin Galili (garin masu neman mafaka don sun yi kisa), Hammon-Dor da kuma Kartan, tare da wuraren kiwonsu, garuruwa uku ke nan.

  24. Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.

  25. Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.