Tsallake zuwa abun ciki

God

11,427 ayoyi · 2 'yan gida

Ayoyin da suka ambaci God

Tace bisa littafi
  1. Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.

  2. Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan ’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.

  3. “Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci ’ya’yansu, ’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?

  4. “Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da ’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.

  5. “Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”

  6. Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.

  7. ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.

  8. Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.

  9. Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.

  10. Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.

  11. Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.

  12. ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.

  13. Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.

  14. Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.

  15. Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.

  16. Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.

  17. Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”

  18. Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.

  19. Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.

  20. Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”

  21. Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;

  22. yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.

  23. Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.

  24. Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.

  25. Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.