God
Ayoyin da suka ambaci God
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma ’ya’yana suna kewaye da ni,
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?