Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Oppression

86 ayoyi · 8 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

Tace bisa littafi
  1. Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su

  2. “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.

  3. “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.

  4. In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.

  5. Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye, ’ya’yanku kuwa su zama marayu.

  6. In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.

  7. Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.

  8. Kada ku zalunci ɗan ƙodago matalauci da mabukaci, ko da shi ɗan’uwanku ne mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a cikin garuruwanku.

  9. Ku biya kuɗin aikinsa kowace rana kafin fāɗuwar rana, domin shi matalauci ne, yana kuma sa rai a kan wannan hakkin ne, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har yă zama laifi a gare ku.

  10. Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.

  11. Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.

  12. Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”

  13. “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.

  14. Kome yawan ’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.

  15. Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.

  16. Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,

  17. abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.

  18. Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.

  19. Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.

  20. Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.

  21. Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.

  22. Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.

  23. Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

  24. Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.

  25. Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,