- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Hypocrisy
Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
(Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
“Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!