Tsallake zuwa abun ciki

circa 6 BC – AD 30

The Life of Jesus

The eternal Son of God enters history: born in Bethlehem, baptized in the Jordan, crucified at Golgotha, raised on the third day.

3,779 ayoyi · 4 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Luka 12:11kusan 33 M.

    “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,

  2. Luka 12:12kusan 33 M.

    gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”

  3. Luka 12:13kusan 33 M.

    Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”

  4. Luka 12:14kusan 33 M.

    Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”

  5. Luka 12:15kusan 33 M.

    Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”

  6. Luka 12:16kusan 33 M.

    Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.

  7. Luka 12:17kusan 33 M.

    Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’

  8. Luka 12:18kusan 33 M.

    “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.

  9. Luka 12:19kusan 33 M.

    Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.” ’

  10. Luka 12:20kusan 33 M.

    “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’

  11. Luka 12:21kusan 33 M.

    “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”

  12. Luka 12:22kusan 33 M.

    Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.

  13. Luka 12:23kusan 33 M.

    Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.

  14. Luka 12:24kusan 33 M.

    Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!

  15. Luka 12:25kusan 33 M.

    Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?

  16. Luka 12:26kusan 33 M.

    Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?

  17. Luka 12:27kusan 33 M.

    “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.

  18. Luka 12:28kusan 33 M.

    In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!

  19. Luka 12:29kusan 33 M.

    Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.

  20. Luka 12:30kusan 33 M.

    Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.

  21. Luka 12:31kusan 33 M.

    Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.

  22. Luka 12:32kusan 33 M.

    “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.

  23. Luka 12:33kusan 33 M.

    Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.

  24. Luka 12:34kusan 33 M.

    Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.

  25. Luka 12:35kusan 33 M.

    “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,