God
Ayoyin da suka ambaci God
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.