God
Ayoyin da suka ambaci God
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin ’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da ’ya’yansu,
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
Ya mai da iska suka zama ’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.