Tsallake zuwa abun ciki

circa 1406–1380 BC

Conquest of Canaan

Joshua leads Israel across the Jordan into the promised land, defeating the Canaanite kingdoms one by one.

658 ayoyi · 1 littafi da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

  1. Yoshuwa 14:15kusan 1444 K.H.

    (Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.

  2. Yoshuwa 15:1kusan 1443 K.H.

    An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.

  3. Yoshuwa 15:2kusan 1443 K.H.

    Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,

  4. Yoshuwa 15:3kusan 1443 K.H.

    zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.

  5. Yoshuwa 15:4kusan 1443 K.H.

    Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.

  6. Yoshuwa 15:5kusan 1443 K.H.

    Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,

  7. Yoshuwa 15:6kusan 1443 K.H.

    wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.

  8. Yoshuwa 15:7kusan 1443 K.H.

    Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.

  9. Yoshuwa 15:8kusan 1443 K.H.

    Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.

  10. Yoshuwa 15:9kusan 1443 K.H.

    Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).

  11. Yoshuwa 15:10kusan 1443 K.H.

    Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.

  12. Yoshuwa 15:11kusan 1443 K.H.

    Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.

  13. Yoshuwa 15:12kusan 1443 K.H.

    Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.

  14. Yoshuwa 15:13kusan 1443 K.H.

    Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)

  15. Yoshuwa 15:14kusan 1443 K.H.

    Daga can sai Kaleb ya kori ’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.

  16. Yoshuwa 15:15kusan 1443 K.H.

    Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).

  17. Yoshuwa 15:16kusan 1443 K.H.

    Kaleb ya ce, “Zan ba da ’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”

  18. Yoshuwa 15:17kusan 1443 K.H.

    Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa ’yarsa, ya kuwa aure ta.

  19. Yoshuwa 15:18kusan 1443 K.H.

    Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”

  20. Yoshuwa 15:19kusan 1443 K.H.

    Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.

  21. Yoshuwa 15:20kusan 1443 K.H.

    Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.

  22. Yoshuwa 15:21kusan 1443 K.H.

    Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,

  23. Yoshuwa 15:22kusan 1443 K.H.

    Kina, Dimona, Adada,

  24. Yoshuwa 15:23kusan 1443 K.H.

    Kedesh, Hazor, Itnan,

  25. Yoshuwa 15:24kusan 1443 K.H.

    Zif, Telem, Beyalot,