God
Ayoyin da suka ambaci God
Duk wanda ya sami mace ya sami abu mai kyau ya kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Wautar mutum kan lalatar da ransa, duk da haka zuciyarsa kan ba wa Ubangiji laifi.
Ana gādon dawakai da wadata daga iyaye ne, amma mace mai basira daga Ubangiji ne.
Duk wanda yake kirki ga matalauta yana ba wa Ubangiji bashi ne, zai kuwa sami lada game da abin da ya yi.
Da yawa ne shirye-shiryen zuciyar mutum, amma manufar Ubangiji ce takan cika.
Tsoron Ubangiji yakan kai ga rai. Sa’an nan mutum ya sami biyan bukata, ba abin da zai cuce shi.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
A hannun Ubangiji zuciyar sarki kamar ruwan rafi ne wanda yake bi da shi duk inda ya so.
Mutum zai yi tunani hanyoyinsa daidai suke, amma Ubangiji yakan auna zuciya.
Yin abin da yake daidai da kuma nagari Ubangiji ya fi yarda da shi fiye da hadaya.
Mai Adalci kan lura da gidan mugu kan kuma zama sanadin lalacin mugu.
Babu hikima, babu tunani, babu shirin da zai yi nasara a kan Ubangiji.
Akan shirya doki domin ranar yaƙi, amma nasara tana ga Ubangiji ne.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.