God
Ayoyin da suka ambaci God
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.