God
Ayoyin da suka ambaci God
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.