God
Ayoyin da suka ambaci God
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu
Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.
Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.
Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.
Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci, Ya Allah Mai Cetonmu, begen dukan iyakar duniya da kuma na tekuna masu nesa,
wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka, bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,
Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka; inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.
Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa; kana azurta ta a yalwace. Rafuffukan Allah sun cika da ruwa don su ba mutane hatsi, don haka ne ka ƙaddara.
Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta; ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.
Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka, amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” Sela
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada ’yan tawaye su tayar masa. Sela
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;