God
Ayoyin da suka ambaci God
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da ’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
Gama Allah bai ba ta hikima ba ko kuma iya fahimta.
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Ba wanda ya isa yă tsokane ta. Wane ne kuma ya isa yă yi tsayayya da ni?
Wane ne yake bi na bashi da dole in biya? Duk abin da yake ƙarƙashin sama nawa ne.
“Ba zan daina magana game da gaɓoɓinta ba ƙarfinta da kuma kyan kamanninta ba.
Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
“Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
“Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.