Tsallake zuwa abun ciki

circa 800–400 BC

The Hebrew Prophets

God speaks through Isaiah, Jeremiah, and the minor prophets—calling Israel to repentance and foretelling the coming Messiah.

3,706 ayoyi · 14 littattafai da aka rufe

Ayoyi daga wannan lokacin

Tace bisa littafi
  1. Amma ta yaya zai huta sa’ad da Ubangiji ya umarta, sa’ad da ya umarta shi don yă faɗa wa Ashkelon da kuma bakin teku?”

  2. Irmiya 48:1kusan 584 K.H.

    Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.

  3. Irmiya 48:2kusan 584 K.H.

    Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.

  4. Irmiya 48:3kusan 584 K.H.

    Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.

  5. Irmiya 48:4kusan 584 K.H.

    Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.

  6. Irmiya 48:5kusan 584 K.H.

    Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.

  7. Irmiya 48:6kusan 584 K.H.

    Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.

  8. Irmiya 48:7kusan 584 K.H.

    Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.

  9. Irmiya 48:8kusan 584 K.H.

    Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.

  10. Irmiya 48:9kusan 584 K.H.

    Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.

  11. Irmiya 48:10kusan 584 K.H.

    “La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!

  12. Irmiya 48:11kusan 584 K.H.

    “Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.

  13. Irmiya 48:12kusan 584 K.H.

    Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.

  14. Irmiya 48:13kusan 584 K.H.

    Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.

  15. Irmiya 48:14kusan 584 K.H.

    “Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’

  16. Irmiya 48:15kusan 584 K.H.

    Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.

  17. Irmiya 48:16kusan 584 K.H.

    “Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.

  18. Irmiya 48:17kusan 584 K.H.

    Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’

  19. Irmiya 48:18kusan 584 K.H.

    “Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.

  20. Irmiya 48:19kusan 584 K.H.

    Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’

  21. Irmiya 48:20kusan 584 K.H.

    An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.

  22. Irmiya 48:21kusan 584 K.H.

    Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,

  23. Irmiya 48:22kusan 584 K.H.

    zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,

  24. Irmiya 48:23kusan 584 K.H.

    zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,

  25. Irmiya 48:24kusan 584 K.H.

    zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.