God
Ayoyin da suka ambaci God
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.