God
Ayoyin da suka ambaci God
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
Ka dogara ga Ubangiji ka kuma aikata alheri; yi zama cikin ƙasar ka kuma more makiyaya mai lafiya.
Ka ji daɗinka a cikin Ubangiji zai kuwa biya bukatun zuciyarka.
Ka sa kanka a hanyar Ubangiji; ka kuma dogara gare shi zai kuwa yi wannan.
Zai sa adalcinka yă haskaka kamar hasken safiya, gaskiyarka kuma kamar rana a tsaka.
Ka natsu a gaban Ubangiji ka kuma jira da haƙuri gare shi; kada ka tsorata sa’ad da mutane ke nasara a hanyoyinsu, sa’ad da suke aikata mugayen shirye-shiryensu.
Gama za a datse mugayen mutane, amma waɗanda suke sa zuciya ga Ubangiji za su gāji ƙasar.
amma Ubangiji yakan yi dariyar mugaye, gama ya sani ranarsu tana zuwa.
gama za a kakkarya ikon mugaye, amma Ubangiji zai riƙe mai adalci.
Kwanakin marasa zarge suna sane ga Ubangiji, kuma gādonsu zai dawwama har abada.
Amma mugaye za su hallaka, Abokan gāban Ubangiji za su zama kamar kyan gonaki, za su ɓace, za su ɓace kamar hayaƙi.
waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka za su gāji ƙasar, amma waɗanda ya la’anta, za a kore su.
In Ubangiji ya ji daɗin hanyar da mutum yake bi, zai sa sawu su kahu;
ko ya yi tuntuɓe, ba zai fāɗi ba, gama Ubangiji yakan riƙe shi da hannunsa.
Gama Ubangiji yana ƙaunar masu aikata daidai kuma ba zai yashe amintattunsa ba. Za a hallaka masu aikata mugunta gaba ɗaya, ’ya’yan mugaye za su hallaka.
Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.
amma Ubangiji ba zai bar su a ikonsu ba ko ya bari a hukunta su sa’ad da aka kawo su shari’a ba.
Ku sa zuciya ga Ubangiji ku kuma kiyaye hanyarsa. Zai ɗaukaka ku ku ci gādon ƙasar, sa’ad da aka kawar da mugaye, za ka gani.
Ceton adalai kan zo daga Ubangiji; shi ne mafaka a lokacin wahala.
Ubangiji yakan taimake su yă kuma cece su; yakan kuɓutar da su daga mugaye yă kuma cece su, domin sukan nemi mafaka daga gare shi.
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.