- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Makoki5
Listen to this chapter
0:00
0:00
Roƙo ga Ubangiji
1
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Hallakar zamantakewa da ta jiki
4
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai ’yantar da mu daga hannuwansu.
9
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Wulaƙanci da rasa mutunci
11
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12
An rataye ’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Rokon mulkin Allah na har abada
19
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note