Skip to content

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da Impenitence: General references

170 ayoyi · 1 fanni

Ayoyi game da General references

Tace bisa littafi
  1. Ubangiji ya ce wa Musa,

  2. “Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.

  3. Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.

  4. Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.

  5. “ ‘In kuka ci gaba da tayar mini, kuka ƙi ku saurare ni, zan ninka wahalolinku sau bakwai, yadda ya dace da zunubanku.

  6. Zan aika da mugayen namun jeji a kanku, za su kuwa kashe ’ya’yanku, su hallaka shanunku, su rage yawanku, ku zama kaɗan. Wannan zai sa a rasa mutane a kan hanyoyinku.

  7. “ ‘In duk da waɗannan abubuwa, ba ku yarda da gyaran da nake yi muku ba, kuka ci gaba da yin adawa da ni,

  8. zan yi adawa da ku, zan kuma aukar muku saboda zunubanku har sau bakwai.

  9. Idan kuma wani mutum ya ji kalmomi na wannan rantsuwa, ya kuma sa wa kansa albarka yana tunani cewa, “Ba abin da zai same ni, ko da na nace a taurinkaina.” Wannan zai jawo lalacewar dukan Isra’ila tare da kai.

  10. Ubangiji ba zai gafarce shi ba, fushinsa da kishinsa za su ƙuna a kan wannan mutum. Dukan la’anonin da aka rubuta a wannan littafi za su fāɗo a kansa, Ubangiji kuwa zai shafe sunansa daga ƙarƙashin sama.

  11. Ubangiji zai ware shi daga dukan kabilan Isra’ila don yă hukunta shi bisa ga dukan la’anonin alkawarin da aka rubuta a wannan Littafin Doka.

  12. Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.

  13. In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.

  14. Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.

  15. Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.

  16. Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,

  17. da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.

  18. “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.

  19. Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.

  20. Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.

  21. Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.

  22. gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.

  23. Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.

  24. Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,

  25. da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,