- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Zabura118
Listen to this chapter
0:00
0:00
Kiran Godiya ga Dukan Mutane
1
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Shaidar Ceto da Amincewa
5
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin ’yantar da ni.
6
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Nasara ta Ikon Ubangiji
15
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Shiga Ƙofofin Ceto
19
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Alkawarin Ƙarshe da Yabon Allah
28
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note