Skip to content
Ƙidaya 34:17-29

Ƙidaya 34:17-29

17
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options