Tsallake zuwa abun ciki

Ayoyin Littafi Mai Tsarki game da The Tribe Of Issachar

13 ayoyi · 20 fannoni

Mahimman ayoyin Littafi Mai Tsarki

  1. A rana ta biyu, Netanel ɗan Zuwar, shugaban mutanen Issakar, ya kawo hadayarsa.

  2. Hadayar da ya kawo ita ce, faranti guda ɗaya na azurfa, nauyinsa shekel ɗari ɗaya da talatin, da kuma daro na yayyafawa na azurfa, nauyinsa shekel saba’in, dukan biyu, an auna su bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, kowannensu cike da lallausan gari, haɗe da mai kamar hadaya ta gari;

  3. ya kuma kawo kwanon zinariya ɗaya mai nauyin shekel, goma cike da turaren hayaƙi;

  4. da ƙaramin bijimi guda ɗaya, tunkiya ɗaya da rago, dukansu bana ɗaya-ɗaya domin hadaya ta ƙonawa;

  5. ya kuma kawo bunsuru ɗaya domin hadaya don zunubi;

  6. da shanu biyu, raguna biyar, bunsurai biyar da kuma ’yan raguna biyar dukansu bana ɗaya-ɗaya, a miƙa su hadaya ta salama. Wannan ita ce hadayar Netanel ɗan Zuwar.

  7. Ƙuri’a ta huɗu ta fāɗa a kan kabilar Issakar, bisa ga iyalansu.

  8. Ƙasarsu gādonsu ta haɗa da, Yezireyel, Kessulot, Shunem,

  9. Hafarayim, Anaharat,

  10. Rabbat, Kishiyon, Ebez,

  11. Remet, En Gannim, En Hadda da Bet-Fazez.

  12. Iyakar ta taɓa Tabor Shahazuma da Bet-Shemesh ta kuma ƙarasa a Urdun. Duka-duka garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.

  13. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon da kabilar Issakar ta samu, bisa ga iyalansu.