- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Umurnin aika ’yan leƙen asiri
Ƙidaya 13:1-16
1
Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
Settings