- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ayuba18
Listen to this chapter
0:00
0:00
Bildad ya tsawata wa maganar Ayuba
1
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Mugaye suna faɗawa cikin tarko na duhu
5
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
Tsoro da hallaka suna jiran mugaye
11
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
Cikakkiyar shafe suna da zuriya
15
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19
Ba shi da ’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note