Skip to content
Mattiyu 24:15-28

Mattiyu 24:15-28

15
“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
16
to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
17
Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
18
Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
19
Kaiton mata masu ciki da mata masu renon ’ya’ya a waɗancan kwanakin!
20
Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
21
Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
22
“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
23
A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
24
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
25
Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
26
“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
27
Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
28
Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options