Skip to content
Ayuba 30:1-10

Ayuba 30:1-10

1
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9
“Yanzu kuma ’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options