Skip to content
Ayuba 30:9-15

Ayuba 30:9-15

9
“Yanzu kuma ’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12
A hannun damana ’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options