Ayuba 29:21-25
21
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.
Settings