Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 29:1-11

Ayuba 29:1-11

1
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma ’ya’yana suna kewaye da ni,
6
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options