- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Ayuba 29:1-11
1
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma ’ya’yana suna kewaye da ni,
6
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
Settings