Skip to content
Ayuba 29:7-17

Ayuba 29:7-17

7
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options