Tsallake zuwa abun ciki

Zabura136

Kiran Godiya ga Ubangiji Maɗaukaki

1
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi. Ƙaunarsa madawwamiya ce.
2
Ku yi godiya ga Allahn alloli. Ƙaunarsa madawwamiya ce.
3
Ku yi godiya ga Ubangijin iyayengiji. Ƙaunarsa madawwamiya ce.

Abubuwan Al’ajabi na Allah Cikin Halitta

4
Gare shi wanda shi kaɗai yake aikata abubuwan banmamaki, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
5
Wanda ta wurin ganewarsa ya yi sammai, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
6
Wanda ya shimfiɗa duniya a kan ruwaye, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
7
Wanda ya yi manyan haskoki, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
8
Rana don tă yi mulkin yini, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
9
Wata da taurari kuma don su yi mulkin dare; Ƙaunarsa madawwamiya ce.

Ayyukan Allah Masu Ƙarfi a Fitowa

10
Gare shi wanda ya kashe ’ya’yan fari Masar Ƙaunarsa madawwamiya ce.
11
Ya kuma fitar da Isra’ila daga cikinsu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
12
Da hannu mai ƙarfi da hannu mai iko; Ƙaunarsa madawwamiya ce.
13
Gare shi wanda ya raba Jan Teku biyu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
14
Ya kawo Isra’ila ta tsakiyarsa, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
15
Amma ya share Fir’auna da mayaƙansa cikin Jan Teku; Ƙaunarsa madawwamiya ce.

Kayar da Sarakuna da Ba da Ƙasa

16
Gare shi wanda ya bi da mutanensa cikin hamada, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
17
Wanda ya buge manyan sarakuna, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
18
Ya karkashe manyan sarakuna, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
19
Sihon sarkin Amoriyawa Ƙaunarsa madawwamiya ce.
20
Da kuma Og sarkin Bashan, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
21
Ya kuma ba da ƙasarsu gādo, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
22
Gādo ga bawansa Isra’ila; Ƙaunarsa madawwamiya ce.

Tanadin Allah ga Dukan Mutane da Jinƙansa Mai Dauwama

23
Shi wanda ya tuna da mu cikin ƙasƙancinmu Ƙaunarsa madawwamiya ce.
24
Ya kuma ’yantar da mu daga abokan gābanmu, Ƙaunarsa madawwamiya ce.
25
Wanda kuma ke ba da abinci ga kowace halitta. Ƙaunarsa madawwamiya ce.
26
Ku yi godiya ga Allah na sama. Ƙaunarsa madawwamiya ce.
Use arrow keys to navigate
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options