Tsallake zuwa abun ciki

Ayuba23

Ayuba yana son ya gabatar da ƙarar sa a gaban Allah

1
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.

Allah yana ɓoye, amma Ayuba ya kasance da aminci

8
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.

Ikon Allah marar canjawa

13
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Use arrow keys to navigate
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options