Tsallake zuwa abun ciki
Nehemiya 11:20-24

Rarraba Mazauna a Garuruwan Yahuza

Nehemiya 11:20-24
20
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options