Yoshuwa 19:40-48
40
Ƙuri’a ta bakwai ta fāɗa a kan kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
41
Ƙasarsu ta gādo ta haɗa da, Zora, Eshtawol, Ir Shemesh,
42
Shalim, Aiyalon, Itla,
43
Elon, Timna, Ekron,
44
Elteke, Gibbeton, Ba’alat,
45
Yehud, Bene-Berak, Gat-Rimmon,
46
Me Yarkon da Rakkon tare da sashen da yake fuskantar Yaffa.
47
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
48
Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan, bisa ga iyalansu.
Settings