Skip to content
Ayuba 15:17-35

Ayuba 15:17-35

17
“Ka saurare ni, zan kuma yi maka bayani; bari in gaya maka abin da na gani,
18
abin da masu hikima suka ce, ba tare da sun ɓoye wani abu da suka samu daga wurin iyayensu ba
19
(waɗanda su ne masu ƙasar kafin baƙi su shigo ƙasar).
20
Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
21
Ƙara mai bantsoro za tă cika kunnuwansa ’yan fashi za su kai masa hari.
22
Yana jin tsoron duhu domin za a kashe shi da takobi.
23
Yana ta yawo, abinci don ungulaye; ya san ranar duhu tana kusa.
24
Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,
25
domin ya nuna wa Allah yatsa ya rena Allah Maɗaukaki,
26
ya tasar masa da faɗa da garkuwa mai kauri da kuma ƙarfi.
27
“Ko da yake fuskarsa ta cika da kumatu kuma yana da tsoka ko’ina,
28
zai yi gādon garuruwan da suka lalace, da kuma gidajen da ba wanda yake zama a ciki, gidajen da sun zama tarkace.
29
Ba zai sāke zama mai arziki ba, dukiyarsa ba za tă dawwama ba, abin da ya mallaka kuma ba zai bazu a ƙasar ba.
30
Ba zai tsere wa duhu ba; wuta za tă ƙona rassansa, kuma numfashi daga bakin Allah zai hallaka shi.
31
Kada yă ruɗi kansa ta wurin dogara ga abin da ba shi da amfani domin ba zai samu wani abu ba daga ciki.
32
Kafin lokacinsa yă cika, za a gama biyansa duka, kuma rassansa ba za su ba da amfani ba.
33
Zai zama kamar itacen inabi wanda ’ya’yansa suka kakkaɓe kafin su nuna, kamar itacen zaitun zai zubar da furensa.
34
Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da ’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
35
Suna yin cikin rikici su kuma haifi mugunta; cikinsu yana cike da ruɗami.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options