Ayuba 15:7-16
7
“Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
8
Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
9
Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
10
Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.
11
Ta’aziyyar Allah ba tă ishe ka ba. Maganarsa mai laushi ba tă ishe ka ba?
12
Don me ka bar zuciyarka ta kwashe ka, kuma don me idanunka suke haske,
13
har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?
14
“Mene ne mutum, har da zai zama da tsarki, ko kuma mace ta haife shi, har yă iya zama mai adalci?
15
In Allah bai nuna amincewa ga tsarkakansa ba, in har sammai ba su da tsarki a idonsa,
16
mutum fa, wanda yake da mugunta da lalacewa, wanda yake shan mugunta kamar ruwa!
Settings