1 Tessalonikawa 5:1-11
1
To, ’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
2
gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
3
Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
4
Amma ku, ’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
5
Dukanku ’ya’yan haske ne da kuma ’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
6
Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
7
Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
8
Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
9
Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
10
Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
11
Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
Settings